RUWAN DUFANA

Allah ya ba mu labarin mutanen farko cikin suratul Ma’ida:

Q5:27 “Karanta musu labarin ‘ya’ya biyu na Adam da gaskiya, lokacin da su ka bada baiko, sai aka karba da ga dayansu kuma ba’a karba da ga dayan ba. Ya ce ”lallai ne zan kashe ka” dayan ya ce “Abin sani dai Allah na karba da ga masu takawa ne” 

Allah ya fara ba mu labarin mutanen farko da nuna cewa su na da addini na bautar Allah wanda har baiko (Sacrifice) su na yi. Dalilin haka domin karyata masana tarihin asalin rayuwa da ke nuna cewa mutanen farko ba su san addini ba, wai sai a lokacin mutanen shu’aibu (Habilis) ne aka fara bauta. A aya ta gaba:

Q5:30-31 “Sai ransa ya kawatar masa da kashe dan’uwansa sai kuma ya kashe shi, sannan ya wayi gari da ga masu hasara. Sai Allah ya aiki wani hankaka, ya na tono a cikin kasa domin ya nu na masa yadda zai binne gawar dan’uwansa. Ya ce “Kaitona na kasa in kasance kamar wannan hankaka domin in binne gawar dan’uwana”

Binciken masana kimiyya ya nuna cewa mutanen farko (Afarensis) sakamakon kasusuwansu da aka tono a nan Afurka, sun rayu a duniya kimanin shekaru miliyan uku da rabi kuma girmansu baya wuce mita daya da rabi. Girman kwakwalwarsu kuwa bai wuce cubic centimetre 350 ba (Wato da kadan ta fi girman kwakwalwar yaro). Qur’ani ya kara mana bayaninsu domin ya tabbatar mana su na da yare kuma su na magana dashi. Sannan kuma su na da addini, sabanin fahimtar masana kimiyya. Qur’ani ya tabbatar mana cewa karfin kwakwalwarsu ya na da rauni, domin a lokacin ba su ma da ilimin binne gawa, kamar yadda sauran dabbobo ke yi sai dai a yasar da ita har ta rube, sai da Allah ya turo hankaka ya nuna masa. Allah dai shi ne mafi sani.

Mutanen da su ka zo bayan wadannan su ne mutanen Nuhu, kuma Allah ya ba mu cikakken labarinsu. Mutanen Nuhu, masana kimiyya na kiransu da Africanus saboda su ma a nan Afurka aka sami kasusuwansu. Babban abinda ya banbanta su da mutanen farko shi ne yadda kwakwalwarsu ta habaka da ga cubic centimetre 350 zuwa c.c. 400. Binciken kashinsu ya nuna cewa sun zauna a duniya kimanin shekaru miliyan biyu da rabi, wato bayan karewar mutanen farko. Labarin Annabi Nuhu da ruwan dufana, labari ne da babu wata al’umma da ba ta da irin nata. Kusan dukkan addinai sun zo da labarin, amma babu inda aka bada labarin da hujjoji na kimiyya kamar Qur’ani. Allah ya fara ba mu labarin cikin suratul Ankabut:

Q29:14 “Lallai, mun aika Nuhu zuwa ga mutanensa. Sai ya zauna a cikinsu shekara dubu face hamsin”

Wata mu’ujiza ta Qur’ani shi ne kalma daya ko biyu na iya kunsar wani fanni guda na ilimi. A wannan aya Allah ya ce Annabi Nuhu ya zauna tare da mutanensa tsawon shekaru 950 kafin ma ayi ruwan dufana. Abu na farko shi ne mun san cewa bayan ruwan dufana ma Nuhu yaci gaba da rayuwa kafin mutuwarsa don haka hakikanin shekarunsa sun fi 950 kenan. Hikimar fada mana iya shekarun Nuhu shi ne domin mu dada fahimtar cewa jinsin mutanensa ba fa irin mutanen da mu ka sani bane, domin tsawon rai (Life span) ya na daga cikin gagaruman abubuwa da su ke banbance jinsuna. Masana kimiyya na amfani da tsawon rai wajen rarrabe azuzuwa na halittu. Misali mutum kamar ni ko kai bama iya rayuwa fiye da shekara 100 zuwa 120, yayin da mutum ya wuce wadannan shekaru ya na zama tamkar ba rayayye ba. Haka nan Biri baya wuce shekaru 40, Giwa ba ta wuce shekaru 80, kare baya wuce 15. Kananan halittu irinsu kuda baya wuce kwana talatin, sauro bai fi sati biyu ba, kwayoyin halitta da ke dakon jini a jikinmu ba sa wuce awa 12. Don haka tsawon rai wani gagarumin abu ne da ke banbance jinsuna (Species). Babbar hikimar da Allah ya sa jinsu nan mutanen farko ke da irin wannan tsawon rai shi ne, na farko dai kwakwalwarsu ba ta habaka sosai ba kuma mutane ba su da yawa a lokacin, idan babu irin wannan tsawon rai sai jinsin Dan Adam ya kare da wuri. Kuma jinsuna masu karanci dadewa sun fi saurin haihuwa. A cikin suratul Hud Allah yaci gaba da labarin Nuhu:

Q11:37-38 “Ka sassaka jirgi bisa ganinmu da wahayinmu kuma kada ka yi mini magana a cikin sha’anin wadanda su ka kafirta. Lallai su wadanda ake nutsarwa ne. kuma ya na sassaka jirgin cikin natsuwa, a ko yaushe shugabanni da ga mutanensa su ke wucewa ta gabansa sai su yi izgili gareshi.”   

Wannan ayoyi na ba mu hasken cewa a wannan lokaci ba’a san sassaka ba don gashi manyan gari ma su na ganin kamar Nuhu ya hauka ce su na yi masa dariya. Kuma Allah ya ce mana ita kanta sassakar jirgin karkashin wahayi Nuhu ke yinta:

Q11:40 “Har a lokacin da umarnin mu ya je, kuma tanda ta bulbula. Mu ka ce ka dauka cikinta da ga kowanne ma’aura guda biyu, da kuma iyalanka face wanda magana ta gabata a kansa, da wanda ya yi imani”

Wannan bala’i na ruwa ba ya faru ya kare bane a wani dan kankanin lokaci, abu ne da ya dauki lokaci mai tsawo. Allah ya umarci Nuhu ya rika diban halittu na dabbobi da tsirrai (maza da mata) da kuma mutane. Saboda ya kaddara ruwan zai halaka ilahirin halittu na wannan zamani ba ma mutane ba kawai. Irin wadannan bala’o’i dasu Allah ke karar da wasu halittu don samar da wasu kamar yadda na yi bayani a baya. Cikin suratul Qamar Allah ya ce:

Q54:11-12 “Sai mu ka bude kofofin sama da ruwa mai zuba. Kuma mu ka bubbugar da kasa ta zama idanun ruwa. Sai ruwa ya hadu a kan wani umarni da aka riga aka kaddara shi”

A sakamakon mamayewar da ruwa ya yi wa doron kasa, sai yanayin duniya ya yi sanyi sosai, ababen da ke dumama duniya kamar zafin rana kuma hadari ya rage shi sosai. Itatuwa kuma da ke fitar da iska su ka kasance karkashin ruwa don haka sai ruwan ya fara daskarewa. Hujjojin tarihi na kimiyya sun tabbatar da samuwar malalen kankara da ga cikin kogin Atalantika har zuwa manyan duwatsun da ke karshen nahiyar arewacin Amurka. Kuma shi malalen wannan kankara (Glaciation), babu gibi tsakaninsa. Akwai kuma malalen da ya tashi da ga Arewacin duniya, wato da ga Greenland da Iceland ya yo gabas har Kiev a kasar Russia daidai gabar kogin Dnieper. A can gabashi kuma aka sami tuddan kankara na Siberia. Nahiyar Antaktika ita ma sai ta daskare gaba daya (Wadda tafi girman nahiyar Turai), kuma tun da ga wancan lokaci ta ke kankara har zuwa yau. A kudancin Amurka da ga duwatsun Andes har zuwa New Guinea akwai kankara. A Afurka wuraren gabashi, tsakiya da yammaci su ma duk sun sami malalen kankara (Sakamakon wannan kankara ne ma aka sami tafkin nan na mu na Chadi). Sannan da ga gabas ta tsakiya har zuwa manyan duwatsun himalayas sun kasance cikin kankara. A takaice ko’ina cikin duniya ya sami wannan daskarewa. A cikin suratul Hudu Allah ya ce:Q11:41 “Ku hau a cikin ta (jirgin Nuhu) da sunan Allah ya yin da ta ke tafiya da ya yin da ta ke tsaye. Lallai ne Ubangijina, hakika mai gafara ne mai jin kai”

Wannan aya na nuna mana cewa bayan wadanda aka saka cikin jirgin Nuhu a lokacin da aka fara ruwa (Wato lokacin da jirgi ke tafiya), a ya yin da ko’ina ma ya zama kankara an ci gaba da ceton halittu (shi ne ya yin da jirgin ke tsaye). Allah ya kammala labarin da cewa:

Q11:44 “Ya kasa ki hadiye ruwanki, kuma ya sama ki kame. Kuma aka fakar da ruwan, kuma aka hukunta al’amarin kuma jirgin ya daidaita a kan judiyyi” 

Ina ne Judi ta ke? Bincike ya nuna min cewa a cikin gundumar Bohtan a kasar Turkiya ta yanzu akwai wani dutse da ake kira da Judi, kusa da garin Jazirat Ibn Umar. Kuma a Kan iyakar Turkiya da Siriya akwai wasu manyan duwatsu da ake kira Ararat wadanda an sami manyan tafkuna na ruwan gishiri kuma ba sa gudana ko’ina. Manyan su ne tafkin Van da Urumiya. Samuwar wadannan tafkuna ya dada tabbatar da ruwan dufana domin babu yadda za’a sami tafkunan ruwan gishiri a lungunan da ba sa kusa da teku, sai dai idan bayan ruwan dufana ne su ka samu sanadiyyar narkewar kankara.

Bayan wannan al’amari dabbobi da dama sun bace har abada sai dai kawai kasusuwansu. Kuma an sami wasu sabbin jinsuna na dabbobi, don binciken kimiyya ya tabbatar da cewa bayan ruwan dufana ne aka sami jakin dawa (Watakila ratsa barbara cikin jirgin Nuhu). A cikin suratul Muminun Allah ya ce Q23:31 “Sannan kuma mu ka kaga wani karni, na wadansu mutane daban,  da ga bayansu”  Bayan karewar mutanen Nuhu sai Allah ya ka ga halittar wadansu mutane da su ke dabam da su. 

 


Comments

Popular posts from this blog

BAKAR TAURARUWA (BLACK HOLES)

RUKUNIN TAURARONMU-RANA

TSUNTSAYE