KUDAN ZUMA

 

Kwari su ne jinsin dabbobi da suka fi kowacce dabba yawa a wannan duniya tamu. Ana samun su a kusan kowacce nahiya, kuma ayyukansu don amfanin rayuwar Dan Adam ba zai misaltu ba. Su ma ba’a bar su a baya ba cikin irin halittun da Allah yayi mana bayanin su cikin Qur’ani. Allah ya kawo mana maganganu a kan kuda, kudan zuma, tururuwa, gizo-gizo da sauransu. Dukkan abinda Allah ya ambata cikin Qur’ani zaka idan kayi bincike tarar daa shi da cikakken tsari na kimiyya wanda kafin zuwan Qur’ani babu wani cikakken bayani na kimiyya a kansa. Bari mu duba kudan zuma, saboda babu wani kwaro da masana kimiyya suka yi bincike a kansa kamar shi. Cikin suratul Nahli Allah yace

Q16:68 “Kuma ubangijinka yayi wahayi zuwa ga kudan zuma cewa “ka riki gidaje daga duwatsu, kuma daga itace, kuma daga abinda suke ginawa

Wannan aya ta fara da tabbatar mana da cewa dabbobi ma ana yi musu wahayi, domin ba don wannan wahayi ba ta ina zasu rika tafiyar da rayuwarsu a tsare kuma cike da ilimi? Shi wannan wahayi kai tsaye Allah ke yi musu shi ba tare da wani manzo ba. Kowacce dabba na samun irin wannan wahayi (shi masana kimiyya ke kira da instinct). Shi kudan zuma ana samun sa ko’ina cikin duniya idan banda kananan tsibirai da ke cikin teku, sassa masu kankara da a kololuwar manyan tsaunuka. Haka nan kamar yadda ayar ta nuna suna gina gidajensu a cikin muhallan da mutane ke zaune. Akwai a kalla jinsuna 20,000 na kudan zuma kuma suna da banbance-banbance saboda akwai masu launin baki, ruwan dorawa,shudi, kore da sauransu. Gidajensu na kasancewa a tsare tamkar unguwa da mutane ke zaune. A cikin shuri na kudan zuma akwai bangarori daban-daban misali akwai fadar sarauniya, gidajen maza da bangaren mata, sannan akwai rumbuna na ajiye zuma, da wurin saka kwai da dakunan jarirai. A sheka guda ta kudan zuma akan sami kudajen zuma 80,000 ko fiye, kuma a tsarin zamantakewar su sun kasu kashi uku. Wato akwi sarauniya, ma’aikata (wadanda mata ne) da kuma mazaje.

Sarauniya ita kadai ke haihuwa a cikinsu, a rana guda tana iya saka kwi 1500 kuma tsawon ran ta ya na kaiwa daga shekara1-3. A siffa ta banbanta da duk sauran kudan zuma, kuma ta kan sadu da maza shida ko fiye da haka. Daga wannan saduwa ba ta sake saduwa da namiji tsawon rayuwarta, amma dukkan maniyyin da suka dura mata tana tara shi cikin wata ‘yar jaka a cikin cikinta. Lokaci-lokaci sai ta rika amfani da shi wajen saka kwai kuma ita ce ke da alhakin zabar ma kwai irin jinsin da zai kasance (wato ya zama sarauniya irinta ko mace ko kuma namiji). Ta na yin haka ne sakamakon wajen da ta ajiye kwai, misali idan wadanda zasu zama sarauniya ne sai ta saka kwan su a cikin wasu kebabbun akusa da aka gina su a saman shekar kuma a rika basu wani kebabben abinci (Royal jelly) har zuwa lokacin da za’a kyankyashe su. Duk irin wadannan kwayaye na zama sarauniya kuma daga kyankyasarsu zuwa balagarsu kwana 16 ne. Su kuma ma’aikata tana saka kwansu ne a wasu akusa da aka gina a dandakwaryar kasa, sannan ana basu wancan kebabben abinci tsawon kwana biyu ne kacal. Ma’aikata na balaga ne bayan kwanaki 21 da kyankyasa. Maza kuma na balaga ne bayan kwana 24. Aya ta gaba ta ci gaba da cewa

Q16:69” Sannan ki ci daga dukkan ‘yayan itace”  

Kamar yadda na fada a baya kudan zuma na da tsarin kaso uku na sarauniya, mata da maza kuma mata sune ma’aikata waoto duk wata hidima ta shuri da ta shafi farautar abinci da kula da rayuwa sune ke aiwatar da ita. A wannan aya sai Allah yayi amfani da wakilin suna na mace (feminine gender) wajen cewa “ki ci” wato anan da matayen kuda zuma Allah ke magana domin dai sune ke gina shekar kanta wajen tsara dakuna da tsabtace su. Abincin kudan zuma shine ruwa mai zaki da ake samu cikin furanni. Kowanne jinsi na kudan zuma akwai akwai irin furannin da suke ci, wannan shi yasa ake samun ruwan zumar da suke samarwa yake banbanta. Akwai zuma farar saka, ruwan kasa, ja, ruwan dorawa da sauransu. Mataen kuda zuma su ne ki fita don nemo irin wannan ruwa su rika tara shi cikin wani holoko da ke cikin makogwaronta idan ta dawo sheka sai masu adana abinci su tare ta sai ta juye musu su kuma sai su kai shi cikin  rumbuna don ajiya. Idan rumbun ya cika sai su shafa masa wani danko da suke samarwa daga jikinsu don like rumbun kada iska ta shiga. Wani gagarumin aiki da kudan zuma ke yi sakamakon yawo daga wannan fure zuwa wancan a yayin farautar fure shine na barbarar tsirrai. Wato a yayin da kudan zuma ta sauka kan wani fure tana zukar ruwan sukari da ke ciki, to kafafuwanta na kwasar kwayoyin maniyyi na wannan fulawa. Idan tayi gaba kuma ta sauka a wani furen da yake mace sai kwayoyin maniyyin su makale a kai, ta haka ta barbari wadannan furanni. A yanzu masana ilimin kwari na cewa sakamakon wannan Barbara da kudan zuma ke yi yana samar da akalla kudin da ya kai kimanin dala biliyan 20. Ayar ta ci gaba da cewa

Q16:69” Saboda haka ki shiga hanyoyin ubangijin ki, suna horarru” 

Hanyoyin da kudan zuma ke bi wajen sadarwa a junansu ko zuwa farautar abinci akwai matukar gwaninta da tsari. Da farko dai ma’aikata a farkon rayuwarsu ana fita dasu daga cikin shuri don koya nusu hanyiyin da ake bi wajen zuwa neman fure da gane hanyar dawowa gida. Suna amfani da rana wajen gane lokaci da kuma nahiyoyi, daga kofar shurin sai su kalli rana don su gane a nahiyar da take, don haka duk nisan da zasu yi suna amfani da wannan kusurwa da rana take don gane hanyar dawowa gida. To idan lokacin damina ne ko na hunturu da wani lokacin xaka ga rana ta bace cikin hadari ko hazo fa? Allah cikin hikimarsa sai ya hore ma idanuwansu iya ganin zaruruwan ultravoilets  dake fitowa daga rana, wadannan zaruruwa na iya ratsa kusan komai ba kamar hasken rana ba. Ta amfani da gane kusurwowin da wadannan zaruruwa suka fada, da haddace su sai kawai su kama gabansu suna la’akarida su har su je inda zasu su dawo, tamkar yadda masu jirgin ruwa ke amfani da compass wajen gane nahiya. Wani abin mamakin kuma shine yayin da wani kudan zuma ya gano wani waje mai furen da ake nema don tsari na adalci maimakon a saka ta gaba ta koma ta nuna wurin sai ta yi musu kwatance. Yadda take kwatancen kuma shine sai suyi da’ira su kewaye ta, ita kuma sai ta fara rawa da zarya da kewaye wadanda kowanne cikin irin abinda take yi yana da labarin da ya ke bayarwa. Kamar yadda kowa ya sani cewa duniya da’ira ce da ke da kusurwa 360, don haka wannan da’ira tasu ta zama kamar taswira. Sai ta fara kewayen da’irar wanda ke sa su rika shakar irin kanshin furen da ta samo, duk sanda ta kewayo sai ta ratsa ta tsakiya ta nufi daya gefen. Saitin layin da ta ratsa zai sanar dasu nahiyar kusurwar da ta je, sannan iya zagayenta na nufin iya nisan wajen daga shurinsu. Idan tayi zarya sama kuma na nufin wajen abincin da ta gano yana sashen da rana take, amma idan tayi zarya kasa kuma na nufin sashen yana sashen da rana ta bari. Wadanda suka kewaye ta suna kallon ta ba wai zuru kurum suke yi mata ba domin su hardace abinda ta ke koya musu sai su rika kwaikwayon duk irin rawa da motsin da ta tayi. Suna kammalawa sai suyi waje “duuu..” don isa wannan waje.

Wani aikin kuma da ma’aikata ke yi shine na kokarin tsabtace da kula da muhallinsu ta hanyar share shi da kuma samar da daidaiton yanayin zafi ko sanyi  (Temperature) cikin shurin. Misali idan a lokacin zafi ne sukan yi kamar wata ‘yar rumfa suyi ta karkada fuka-fukansu a matsayin fanka domin su kori iska mai zafi don shurin ya huce haka kuma a lokacin hunturu suna yin cincirindo su zama kamar bargo sai su lullube jarirai da kwayayensu, su kuma kasancewa a waje guda suna samun dumin juna. A kowanne lokaci suna kokarin daidaita yanayin sheka ya kasance baya gaza ko wuce mizanin 33.9 a ma’aunin zafi na centigrade, don shine iya dumin da kwayaye ke bukata kafin su kyankyashe. A cikin ayar dai sai Allah ya ce

Q16:69” Wani abin sha yana fita daga cikunanta, mai sabawar launuka, a cikinsa akwai wata warkewa ga mutane”

Sakamakon banbance-banbance na ire-iren furannin da suke ci, shine ya samar da launuka daban-daban na ruwan zuma. Ana samun fara ko ruwan dorawa ko ruwan kasa da sauransu. Dandano kalilan ke kai zuma wajen zaki da dadi, wannan ya sa Mutane suka samar da hanyoyi da dama na sarrafa zuma a matsayin abin sha ko ci. Babu wani abin sha da kan iya dadewa ba tare da an saka masa sindarin hana lalacewa ba kamar zuma, don ta kan kai shekaru a aje ba tare da ta lalace ba. Wannan ya biyo bayan kasancewar a cikin zuma akwai sinadarin da ke yaki da kwayoyin cuta (Wato Antibiotics) irinsu bacteria da ke saka funfuna ko lalacewar abinci kai har ma da kwayar Virus. Kwayoyin cuta na bacteria da virus sune ke haddasa kusan kashi casa’in na cututtukan da ke duniya. A yanzu ana amfani da zuma wajen yaki da cututtuka irinsu na kwanji, jijiyoyi da abin da ya shafi garkuwar jiki, ina ganin da masana ilimin magunguna zasu zurfafa bincike watakila su gano hanyar magance kanjanmau.

Zuma na da dafi wanda take amfani dashi don kariyar kanta daga abokan gaba, a duk lokacin da wata halitta take barazana gareta to sai su buga kugen yaki su far mata da harbi har sai sun hallaka ta ko sun koreta. Shi kansa wannan dafi nata, masana harkokin harhada magunguna na zakulo shi don su cire wani sinadari da ke maganin ko wane irin dafi. Daga karshe sai Allah ya ce

Q16:69” Lallai ne a cikin wannan, Hakika akwai ayoyi ga mutane wadanda suke yin tunani”

A cikin ayoyi biyu kacal Allah ya dunkule mana irin ilimin rayuwar kudan zuma, wanda ke cike da bayanai na gwaninta da suke nuna isa da kwarewa ta Allah. Kuma kamar yadda na fada a baya babu wani kwaro da masana suka yi bincike a kansa kamar kudan zuma domin an rubuta daruruwan littattafai da kasidu a kansa. Allah a cikin Qur’ani ko da yaushe yana jan hankalin mu da mu yi tunani, domin dai tunani shine ya banbanta mu da sauran dabbobi amma kash sai dai a yau al’ummar musulmi mune koma baya wajen bincike da nazari wanda shine irin tunanin da Allah ke ta umartar mu. Allah ya sa mu gane domin mu koma kan matsayin mu na ja gaba tun asali.

 

 

 

Comments

Popular posts from this blog

HUJJOJIN TASHIN KIYAMA A KIMIYANCE

RUWAN DUFANA

QUR’ANI DA KIMIYYA