RAI/RUHI DA MUTUWA


 

Menene Rai ko Ruhi? Wannan tambaya ce da ta shige ma Dan Adam duhu tun farkon halittarsa. Daidaikun mutane da Addinai da dama sun yi iya kokarinsu wajen ganin sun gano bakin zaren wajen fahimtar rai. Amma babu wani addini da ya iya kawo cikakken bayani kafin zuwan musulunci. Kafiran Makka, Yahudawa da Nasara na kalubalantar Annabi da ya kawo musu mu'ujiza kamar yadda Allah ya bamu labari cikin Suratul Ankabut

 

Q29:50 "Kuma su ka ce "Don me ba'a saukar masa da ayoyi (na mu'ujiza) daga ubangijinsa"

 

Sai Allah ya ba su amsa a cikin aya ta gaba inda ya ce

 

Q29:51" Shin bai ishe su ba cewa lallai mu, mun saukar da littafi a kanka, ana karanta shi a kansu"

 

Allah na tabbatar mana da cewa Annabi bai zo da wata mu'ujiza face Qurani ba, domin dai shi ummiyi ne wato bai iya karatu ba ballantana rubutu amma ya zo da littafin da ke kunshe da ilimi na kowanne fanni wanda ba'a taba jin irinsa ba, kuma ba za'a taba ji ba. An saukar da wannan littafi a guggutsure tsawon shekaru 23 amma babu wata aya guda da aka saukar a shekarar farko a Makka wadda zata ci karo da wata ayar da aka saukar bayan shekaru ashirin a madina. Kuma kama daga fannin zamantakewa zuwa nahawu, kimiyya, tarihin mutum da asalin halitta babu inda aka bari a baya. Allah y ace

 

Q6:38 “Ba mu yi sakacin barin komai ba cikin littafi”

 

 A cikin karni na bakwai sanda aka saukar da littafin, duniya na cikin duhun jahilci domin dai addinan yahudu da nasara sun gurbace an yi watsi da ainihin koyarwar littatafan. Amma kasancewar duk da haka babu wanda yafi Yahudu da Nasara ilimi a wannan zamani sai suka fara kalubalantar Annabi da tambayoyi na ilimi. Akwai jerin tambayoyi, musamman guda uku da suka ce in dai shi annabi ne lallai zai iya ba su amsa saboda sun dade su na son amsoshin wadannan tambayoyi kuma an ce musu sabon annabin da zai zo shine kadai zai iya basu cikakkiyar amsa. Lokacin da su ka zo su ka mika wadannan tambayoyi guda uku ga annabi sai ya ce musu su dawo gobe zai ba su amsa. Kasancewar Allah na son mu fahimci mahimmancin sa a rayuwar mu kuma ya nuna mana cewa Annabawa ma na iya yin kuskure ko da yake kuskuren su ba na zunubi ba ne, kuma ba sa gushewa sai Allah ya kautar da su daga wannan kure. Dalilin haka sai ya ki sanar da annabi amsoshin tambayoyin har tsawon makonni ta yadda kafirai suka rika zunden annabi suna cewa ai makaryaci ne. Dalilin wannan ne Allah ya ja masa kunne a cikin suratul Kahaf 

 

Q18:23 " Kada ka ce a game da komai "lallai ne gobe zan yi"

 

Daya daga cikin tambayoyin da su ka yi ita ce, Menene Rai ko Ruhi? Cikin suratul Isra sai Allah ya ba da amsar

 

Q17:85"Su na tambayarka game da ruhi ka ce "Ruhi daga al'amarin ubangijina ne. kuma ba a ba ku (komai) ba daga ilimi face kadan"

 

Tun da Allah ya halicci duniya zuwa yanzu babu wani mahaluki da zai ce ya fahimci yadda rai ya ke domin dai iliminsa kadan ne Allah ya sanar da mu. Shi rai wani kebabben muhalli ne na Allah domin shine sirrin rayuwa kuma shi ne ke tabbatar da cewa babu wani mahalicci sai Allah. Na farko dai daga wajen Allah rai ya samo asali kamar yadda ya bamu labari cikin suratul Hijiri yayin da Allah ya shirya halitta a doron kasa kuma ya ke bai wa mala'iku labari cewa 

 

Q15:29" To idan na daidaita shi (wato Adam) kuma na hura Ruhina a cikinsa to ku fadi gareshi kuna masu sujada"  

    

Ruhi ya samo asalinsa daga ubangiji domin ruhin ubangiji da ya hura ga Adam shine asalin rayuwa a wannan duniya tamu, haka kuma kowanne mahaluki ba ya samuwa sai daga wannan ruhi na ubangiji kamar yadda ya ce mana cikin suratul Sajda

 

Q32:8-9" Sannan ya sanya yayansa daga wani asali na wani ruwa walakantacce. Sannan ya daidaita shi kuma ya hura a cikinsa daga ruhinsa , kuma ya sanya muku ji da gani da zukata. Godiyarku kadan ce kwarai"  

 

Don haka kowannen mu ba zai iya samuwa ba sai daga wannan ruhi da Allah ke busawa daga gareshi, wannan shi ya sa ruhi ya fi karfin duk wadansu hanyoyi na sadarwa da Allah ya hore mana, domin ba ma iya jinsa, dandanarsa, ganinsa ballantana ma mu taba shi. Kawai dai muna iya sanin yana nan ko kuma baya nan ta hanyoyin gane abu rayayye da matacce. Duk inda mai rai yake sai mu san akwai rai kuma duk inda matacce ya ke mun san cewa rai ya fita. Ilimin ruhi kalilan ne Allah ya sanar da mu. Allah ya kalubalanci dukkan halittu da cewa wanda duk yace akwai Allah bayan Allah to hanya guda daya tilo da za'a banbance allolin karya da Allah na gaske shine kamar yadda ya ce mana cikin Suratul Hajj

 

Q22:73" Ya ku mutane ga wani misali, sai ku saurara zuwa gareshi, lallai wadanda kuke kira baicin Allah, ba za su iya halitta kuda ba, ko da sun tattaru (da taimakon juna) domin hakan" 

 

Don haka idan da wani wanda zai iya halittar kuda to bismillah, kuma in har ya iya yi, to za mu sallama masa, amma babu wanda zai iya, domin Allah ya boye wannan ilimi domin ya tabbatar wa masu imani cewa shi kadai ne “iIah”. Masana kimiyya tsawon shekaru sun yi iya kokarinsu wajen samar da halitta mai rai daga abubuwa mara sa rai amma sun kasa kamar yadda suka tabbatar cikin kundin nazarin kimiyyar halittar rayuwa (Encyclopaedia of Biological science) cewa "Dukkan wani kokari na samar da halitta mai rai kai ko ma wani sashe na halitta mai rai daga abubuwa marasa rai ta hanyar binciken kimiyya ya ci tura" Cikin fitattun masana kimiyya da su ka bata shekaru wajen binciken sama da halitta mai rai, akwai Stanley Miller wanda bayan gazawa ga abinda y ace “Hakika gano yadda rai ya samo asali ya kasance wata matsala da tabbata gagararriya fiye da yadda ni da mutane da dama su ka dauka”. Haka nan Simon Conway shi ma cewa ya yi “Hakika an kasa samar da rai a dakin bincike, kuma babu wata alama da cewa za’a iya yi nan gaba…samuwar rai wani al’amari ne gagara misali, sai dai kawai mu ce samuwar rai mu’ujiza ce”. Abokin binciken Stanley Miller, wato Francis Crick wanda su ka yi shekaru gwammai na wannan bincike shi ma cewa ya yi “Duk wani mai fadar gaskiya, da yak e da ilahirin ilimin da muke da shi a yanzu, zai sallama cewa hakika yadda rai ya samu a doron kasa abu ne da kawai sai dai a kira shi da mu’ujiza” Don haka duk yadda mu ka kai ga ilimi ba zamu iya gane sirrin rai ko ruhi ba face dan kalilan da Allah ya sanar da mu.  Rai abokin tagwaitar mutuwa ne, saboda duk lokacin da babu guda akwai gudan. Shi kuma ruhi tun sanda Allah ya fara halittarsa yana nan a raye sai dai kawai yana bayyana ne a matsayin rai a lokacin da aka hada shi da jiki amma da zarar an cire shi daga jiki sai ruhin ya kasance a matsayin mutuwa. Shi yasa Allah ya ce mana cikin suratul Baqara

 

Q2:28" Ya ya kuke kafirta da Allah, alhali kun kasance matattu sai ya rayar da ku, sannan ya sanya ku ku mutu sai ya sake rayar daku, kuma gare shi zaku koma"

 

Wato dukkan mu zamu fuskanci mutuwa biyu da rayuwa biyu. Domin bayan Allah ya halicci dukkan rayuka kuma ya shaidar da su kan mulkinsa sun kasance a yanayi na mutuwa kafin a hada kowanne ruhi da gangar jikinsa (mutuwar farko). Da zarar jiki ya sami ruhi sai ya zama rayaye (rayuwar farko) sannu a hankali kuma sai kowanne mai rai ya dandani mutuwa (mutuwa ta biyu) sannan a lahira kuma ranar tashin kiyama sai a busa wa kowa rai (rayuwa ta biyu kenan). Saboda irin kauna da Allah ke wa bayinsa bai bar mu cikin duhu ba don haka don yana son mu fahimci rayuwa da mutuwa sai ya tsara mu kamar haka

 

Q39:42 "Allah ne ke karbar rayuka a lokacin mutuwarsu, wadanada ba su mutu ba kuma (ya karba ) a cikin barcinsu. Sannan ya rike wanda ya hukunta mutuwa a kansu, kuma ya saki ragowar zuwa ga ajali ambatacce. Lallai a cikin wannan akwai ayoyi ga mutane masu yin tunani"

 

Kamar yadda bahaushe ne ke cewa "Barci kanin mutuwa". Wato a lokacin kowanne barci ana yin 'yar karamar mutuwa ne don Allah na karbar rai ne sai barci ya kwashe ka. Wanda duk lokacin barcinsa ya dace da na ajalinsa shi ke nan babu tashi sai dai ya yi tazarce, amma wanda ke da sauran kwana sai a mayar masa da ran sa ya farka. Shi barci babu wanda zai ce ya san takamaimai lokacin da zai dauke mutum sai dai kawai ya sace ka, kamar yadda mutuwa ita ma bata sallama sai dai ta zo bagatatan. Haka nan ita ma farkawa baka sanin zuwanta sai dai wani abu ya farkar da kai kwatsam. Saboda haka barci da farkawa abubuwa ne guda biyu da Allah ya halitta a jikin mu don su tabbatar mana da cewa lallai akwai mutuwa da tashin kiyama wato barci tamkar mutuwa haka nan farkawa tamkar tashin kiyama. Allah y aba mu labarin cewa

 

Q36:52 “Su ka ce “Ya bonenmu! Wanene ya tayar da mu daga barcinmu?” wannan shine abinda mai rahama yay i wa’adi da shi kuma mazanni sun yi gaskiya”

 

Wato mutuwa tamkar barci ta ke kamar yadda wannan aya ke bamu labarin cewa a ranar lahira kafirai idan an tashe su a rayuwa ta biyu bayan wannan, sais u yi korafin wa ya tashe su daga barcinsu, wato mutuwarsu. Wani gagarumin abu da Allah ya ta'allaka da barci kuma shine Mafarki, shi mafarki ba a banza aka hore mana shi ba sai don Allah ya dada tabbatar mana da cewa duk abubuwa da annabawa su ka zo dashi don kira da gargadi da sakamakonsu gaskiya ne (wato yadda rayuwar lahira za ta kasance). A cikin mafarke-mafarken mu, duk da cewa muna kwance a wani gefe guda sai rayukanmu su rika yin abubuwa na ban mamaki da a zahiri ko kusa ba za mu iya yi ba. Haka nan muna iya jin dadin gaske a mafarki (cin abinci ko jima'i ko farin ciki) ko kuma mu fuskanci matsananciyar wahala (yunwa, asara ko fargaba) yadda muna farkawa za mu ci gaba da jin abinda  ya faru a mafarkin kafin mu gane cewa ashe mafarki ne. A takaice dai Allah na son mu fahimci cewa barci, mafarki da farkawa a kullum rana da Allah ya wajbata a tsarin rayuwarmu, an yi su ne domin su rika tuna mana ko jaddada mana rayuwar duniya, mutuwa da rayuwar lahira ne.  

 

Comments

Popular posts from this blog

HUJJOJIN TASHIN KIYAMA A KIMIYANCE

RUWAN DUFANA

QUR’ANI DA KIMIYYA